7 Yuni 2015 - 18:19
Ana zaben Majalisar Dokoki a kasar Turkiyya

A wannan lahadi sama da mutane milyan 53 ne ke jefa kuri’unsu a zaben ‘yan majalisar dokokin kasar Turkiyya, zaben da ake kallo a matsayin zakaran gwajin dafi ga shugaba Racep Tayyip Erdogon, kasantuwarsa zaben majalisa na farko da ake gudanarwa tun bayan da ya karbi ragamar shugabancin kasar.

Jam’iyyar Erdogon dai na bukatar kujeru 330 daga cikin 550 domin ci giaba da kasancewa mai rinjaye a cikin zauren majalisar.

To sai dai manazarta al’amurran siyasar kasar ta Turkiyya na ganin cewa ko a wannan karo jam’iyyar AKP ta shugaban za ta iya yin nasara a zaben.288